Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Gwamnatin Kano za ta rage kasafin kudin 2020

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata rage kasafin kudin shekarar 2020 da kaso 30 cikin 100.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi yayin wani taron manema labarai da fadarsa ta shirya a Kano.

Gwamnan ya ce sun dauki matakin ne sakamakon kalubalen da ya tunkaro saboda cutar Coronavirus.

A cewar gwamnan nan gaba kadan zasu mika bukatar hakan gaban majalisar dokokin jihar domin sake yin nazari da kuma sahalewa.

Abdullahi Umar Ganduje ya kuma yabawa ‘yan jaridu bisa yadda suke bayar da gudun mowa wajen wayar da kan jama’a game da cutar Covid-19.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!