Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Masari ta ayyana gobe Alhamis a matsayin ranar hutu ga ma’aikata

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina, ta ayyana gobe Alhamis 26 ga Janairu a matsayin ranar hutun ma’aikata a dukkanin kananan hukumomin jihar domin shirin tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Hakan na cikin wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar noma da walwalar jama’a Alhaji Sani Kabomo ya fitar ga manema labarai a yau Laraba.

Ya ce, an bai wa ma’aikata hutun ne domin su yi shirin tarbar shugaba Buhari da zai kai ziyara jihar domin kaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar Aminu Bello Masarai ya samar.

Sai dai ya ce, hutun bai shafi wadanda suke aiki karkashin gwamnatin tarayya ba, da bankuna har ma da masu ayyuka na musamman.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!