Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya za ta bude filayen jiragen saman Kano da Abuja

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce za ta bude filayen jiragen saman kasar nan a ranar takwas ga watan Yulin 2020.

Ministan sufurin sama Hadi Sirika ne ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter, inda ya ce filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas da na Nnamdi Azikwe da ke Abuja za su fara aiki ne ranar takwas ga watan na Yuli.

A cewar sa filayen jiragen sama na Kano, Port Harcourt, Owerri da Maiduguri za a bude su ne ranar 11 ga watan Yulin.

Wannan na zuwa ne bayan sama da watanni uku da gwamnatin tarayya ta rufe filayen jiragen sama, sakamakon annobar Covid-19.

Hadi Sirika ya ce za a bude sauran filayen jiragen saman a ranar 15 ga watan Yuli, sai dai batun fara jigilar jirage zuwa kasashen waje sai a nan gaba kadan gwamnati za ta sanar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!