Connect with us

Manyan Labarai

Majalisar dinkin duniya ta yi Allah-wadai da harin ‘yan Boko Haram

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan kungiyar Boko Haram suka yi wa wasu ma’aikatan bayar da agaji guda biyar a jihar Borno, bayan kama su a Munguno cikin watan Yunin da ya gabata.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban jami’in bayar da agaji na majalisar dinkin duniya a Najeriya Mr Edward Kallon ya fitar a jiya, yana mai nuna kaduwarsa da yadda ‘yan Boko Haram din suka hallaka ma’aikatan na su.

Edward Kallon ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan da sauran ‘yan uwa da abokan aikinsu.

A jiya laraba ne dai kungiyar Boko Haram ta fitar faifan bidiyon yadda suka kashe ma’aikatan agajin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!