Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Muhammad Garba ya ja hankalin ‘yan jaridu

Published

on

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano kwamaret Muhammad Garba ya ja hankalin kungiyoyin ‘yan jaridu na gidajen rediyoyi dasu mayar da hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa gaskiya da adalci.

Kwamishinan yayi wannan kira ne ta bakin shugaban kungiyar ‘yan jaridu ta kasa reshen jihar Kano Kwamaret Abbas Ibrahim wanda ya wakilci kwamishinan yayin rantsar da sabbabin kungiyar ‘yan jaridun gidajen rediyo na Kano.

Abbas Ibrahim ya ce ‘yan jarida suna da muhimmanci a rayuwar al’umma domin suna kokari wajen gano matsalolin dake damun al’umma a kowane mataki.

Gwamnatin Kano ta rinka baiwa ‘yan jaridu hadin kai- Ammai Mai Zare

DW na bada horo ga ‘yan jaridu a Abuja

Nassarawa:An sace tare da garkuwa da mai dakin shugaban kungiyar ‘yan jaridu

A nasa jawabin sabon Shugaban kungiyar ‘yan jaridun gidajenn rediyo na Kano, Nura Bala Ajingi ya ce zai yi kokari wajen ganin ya sauke nauyin da aka dora masa.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa ‘yan jaridu da dama ne daga gidajen rediyoyi daban-daban na Kano suka halarci taron.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!