Connect with us

Labarai

Mutane 10,000 ne suka kamu da cutar mashaƙo a 2026- NCDC

Published

on

Cibiyar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta ce sama da mutane 10,000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar mashaƙo a 2026.

Darakta-Janar na NCDC, Dakta Jide Idris, ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a wani taron manema labarai kan halin da ake ciki game da barkewar cutar kwalara da mashaƙo a Najeriya.

Sai dai Dakta Idris ya ce an samu raguwar masu kamuwa da cutar kwalara a farkon shekarar nan, idan aka kwatanata da 2025.

Dakta Idris ya ce an samu rahoton sama da mutum 65,000 da ake zargin sun kamu da kwalara a jihohi 35 da kuma kusan ƙananan hukumomi 195 a bana, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Dakta Idris ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen ɗaukar matakan dakile barkewar cututtukan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!