Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Wani mutum ya rasu bayan ya killace kansa a Kano

Published

on

Wani magidanci a unguwar Gwammaja dake nan Kano ya rasu, bayan ya killace kansa a gidan sa dake unguwar.

Magidanci da har izuwa yanzu ba a bayyana sunan sa ba, ya killace kansa ne tsawon kwanaki uku bayan ya dawo daga birnin tarayya Abuja.

Wakilin mu Abba Isah Muhammad ya rawaito mana cewa jami’an ma’aikatar lafiya ta jihar Kano sun hallara a unguwar ta gwammaja dauke da kayayyakin aiki na musamman domin bincike da daukar gawar.

Sai dai Kansilan lafiya na karamar hukumar Dala Ibrahim Garba ya shaidawa Freedom cewa, sakamakon bincike jami’an lafiya ke tsaka da gudanarwa a halin yanzu, nan una cewa mutuwarsa na da alaka da bugun zuciya.

Cikakken labarin zai zo muku a shirin Inda Ranka na yau da karfe 9:30 na dare

Karin labarai:

 An tantance mutane 46 a Kano kan Coronavirus

Covid19: Ana dab da kammala ginin cibiyar killacewa da Dangote ke ginawa a Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!