Labarai
Yan bindigar da suka tsere daga wasu yankunan Nijeriya sun yiwa Birnin Gwari kawanya
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/09/yan-bindiga.jpg)
Kwanaki kadan bayan labarin cewa ‘yan bindigar da suka tsere daga wasu yankunan na kutsawa cikin garin Birnin-Gwari da ke jihar Kaduna.
Mazauna garin sun ce tun daren ranar Alhamis ne ‘yan bindigar suka kewaye da garin na Birnin-Gwari tare da yin awon gaba da jama’a da dama.
Wata majiya ta ce, al’amarin ya faru ne a unguwar Gobirawa da ke cikin garin Birnin-Gwari da ke kusa da gidan talabinjin na kasa wato NTA Birnin-Gwari da ke da nisan sama da mita 500 daga sansanin sojin sama.
Tuni dai Majalisar Karamar Hukumar Birnin-Gwari ta yi gargadi ga mazauna yankin da su takaita zirga-zirga a daukacin masarautar Birnin-Gwari.
Rahoton: Abdulkadir Haladu Kiyawa
You must be logged in to post a comment Login