Tsaro
Yan sanda sun kama mutum uku kan zargin aikata kisan gilla a Bauchi

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutum uku da ake zargi da hannu a kisan gilla da aka yi wa wasu maza biyu a kauyen Bunga da ke karamar hukumar Warji ta jihar.
Kakakin rundunar, CSP Nafiu Habib, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 7 ga Mayu, 2026 bayan samun kiran gaggawa cewa wasu mutane na bin wasu da zargin su da sata. Wadanda aka kashe sun hada da Kabiru Idris mai shekaru 30 da Ibrahim Samaila Danliti mai shekaru 40, duk daga kauyen Gabanga a Warji, inda ake zargin taron jama’a daga karamar hukumar Ningi sun bi su suna ihu da “barayi” har suka tare su tare da yi musu dukan tsiya.
An garzaya da su Asibitin Karamar Hukumar Warji domin ceto rayukansu, sai dai likita ya tabbatar da rasuwarsu.
‘Yan sanda sun ce sun kama Samaila Turawa, Danbaba Haruna da Ubale Mai Kaji bisa zargin hannu a lamarin, yayin da ake ci gaba da farautar sauran wadanda suka tsere.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya yi Allah wadai da kisan tare da umartar gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da an hukunta duk masu hannu a lamarin.
You must be logged in to post a comment Login