Connect with us

Labaran Wasanni

‘Yan wasan Tunisia biyu sun kamu da COVID-19

Published

on

‘Yan wasan kasar Tunisia biyu Ferjani Sassi da Seifeddine Khaoui sun kamu da cutar COVID-19.

An gudanar da gwajin cutar ne kan ‘yan wasan bayan fafatarwar su da Sudan a ranar Juma’ar makon jiya.

A dai gobe Talata ne Najeriya take shirin hadu da kasar ta Tunisia a wasan sada zumunta da ake gudanarwa a Austria.

Hakan zai zama kalubale ga tawagar ta Tunisia sakamakon kamuwar ‘yan wasan biyu, yayin da aka cire su daga cikin tawagar kasar.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa,“Tuni dai aka zare ‘yan wasan biyu daga cikin wadanda zasu fafata da Najeriya a gobe Talata”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!