Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

Yanzu-yanzu: Gwamnati ta bada umarnin rufe makarantu a Jigawa

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta bada umarnin rufe makarantun Firamare da Sakandiren jihar bakiɗaya.

Mai riƙon muƙamin babban sakataren ma’aikatar ilimi da kimiyya ta jihar Alhaji Rabi’u Adamu ne ya sanar da hakan da yammacin Talata.

Alhaji Rabi’u Adamu ya ce, rufe makarantun ya shafi makarantu gwamnati da ma masu zaman kansu.

Sai dai bai bayyana dalilin rufe makarantun ba.

Amma tuni al’umma suka fara bayyana mabanbanta ra’ayoyi inda wasu ke danganta hakan da sace ɗaliban Sakandiren Ƙanƙara a jihar Katsina.

Wasu kuma na alaƙanta hakan da dake ɓarkewar annobar Corona.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!