Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Akwai yiwuwar Ganduje ya ‘karawa ‘yan kasuwa ranakun sararawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta ce zata karawa ‘yan kasuwa kwana guda matukar sun bi dokar da aka gindaya musu kan Covid-19.

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ce matsawar ‘yan kasuwar suka bawa gwamnati hadin kai shakka babu akwai yuwuwar a kara musu kwana gudan da suka nema tun farko.

Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da jagorancin tawagar masu feshin magani a kasuwar sabon gari da ke birnin Kano, a wani bangare na tunkarar cutar Coronavirus da ma sauran cutuka masu yaduwa a jihar.

“Fatan mu shine mu kakkabe annobar Covid-19 da ma sauran cutuka masu yaduwa a jiharmu, don haka muna bukatar goyon baya daga al’ummar jihar”. a cewar sa

Gwamnan ya kuma kara bawa al’ummar Kano hakurin zaman gida da suke yi, inda yace hakan wani mataki ne na dakile yaduwar annobar Covid-19 a tsakanin mutanen Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!