Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar EFCC ta mikawa jami’ar Dutsinma motocin sata

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa wato EFCC , reshen jihar Kaduna ta mika motoci guda hudu da ta kwato  daga hannun wasu hukumomin jami’ar tarayya ta Dutsinma dake jihar Katsina ga hukumomin jamia’ar.

Mai magana da yawun hukumar  Mr Wilson Uwujaren ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a Abuja , ya ce an samo motocin ne biyo bayan takarda da ministan ilimi Malam Adamu Adamu ya fitar.

Mr Uwujaren yace ministan yana zargin wasu daga cikin shugabannin jamia’ar da biyan kansu wasu miliyoyin kudade a matsayin alawus , tare da sanya kansu wasu ayyukan da ake zarginsu da cin hancin da rashawa ta hanyar amfani da bankin First bank.

Wasu daga cikin laifukan da ake zarginsu da shi sun hadar da almundahana wajen sayo kayayyakin aiki da kara kudadensu ta hanyar kara farashi, da kuma baiwa wasu kwangiloli ta hanyar hadin baki da kara kudade.

Hukumar EFCC ta cafke masu kamfanin boge da bindigu a Kano

Kayayyakin da aka kwato sun hadar da wasu motoci Toyota corolla guda biyu mai dauke da lamba FUDMA 51F -03FG da FUDMA 51F-05FG, sai wata Toyota Land Cruiser ZTRJ150L mai dauke da lamba FG 668 – E45 da kuma Toyata Camry XLE 205 da kuma ABC 601 LX.

Da yake mika kayayyakin, shugaban hukumar EFCC reshen jihr Kaduna Mailafia Yakubu  ya ce an saki motocin ne biyo bayan bukatar jami’ar na sakar motocin.

Ya ce mika musu motocin na daga cikin irin ayyukan da hukumar

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!