Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar INEC ta kara wa’adin karbar katin zabe

Published

on

  • INEC ta karin wa’adin mako guda
  • Karin wa’adin zai bada dama ga wadanda ba su karbi nasu ba

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, ta sanar da yin karin wa’adin mako guda a bisa ranakun da za a kammala karbar katin yin zaben a cibiyoyin hukumar a fadin Najeriya.

Mai magana da yawun hukumar INEC a Kano Adam Ahmad Maulud, ne ya sanar da hakan a zantawarsa da Freedom Radio a safiyar yau.

Adam Ahmad Maulud ya ce, karin wa’adin zai bada dama ga wadanda ba su karbi na su ba, su je su karba kafin cikar wa’adin.

 

Rahoton: Hafsat Abdullahi Danladi

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!