Connect with us

Labarai

Mbappe ne kan gaba wajen lashe kyautar Golden Boot a gasar kofin duniya

Published

on

Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya (FIFA) ta tabbatar da cewa kyaftin ɗin Faransa, Kylian Mbappé, shi ne ke kan gaba a takarar lashe kyautar adidas Golden Boot, duk da cewa shi da kyaftin ɗin Argentina, Lionel Messi, sun zura kwallaye takwas kowannensu bayan kammala wasannin kwata fainal na gasar cin kofin duniya ta 2026.

 

Mbappé ya koma matsayi na farko bayan ya ci kwallonsa ta takwas a wasan da Faransa ta doke Morocco, inda yanzu yake da kwallaye takwas da kuma taimakawa aka ci uku. Messi ma yana da kwallaye takwas, amma ya bayar da taimako biyu kacal, lamarin da ya sa yake biye da ɗan wasan na Faransa. Ɗan wasan Norway, Erling Haaland, na matsayi na uku da kwallaye bakwai, yayin da Jude Bellingham da Harry Kane suke da kwallaye shida kowannensu.

 

FIFA ta ce idan ‘yan wasa biyu ko fiye suka kammala gasar da adadin kwallaye iri ɗaya, za a fara duba yawan taimakon da suka bayar wajen cin kwallo. Idan har yanzu suka yi kunnen doki, za a duba wanda ya buga mintuna kaɗan a gasar, inda shi ne zai fi samun matsayi. A halin yanzu, Mbappé ya buga mintuna kaɗan fiye da Messi, abin da ya ba shi damar ci gaba da jagorantar tseren neman kyautar Golden Boot.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!