Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wasu marasa tarbiyya, ba arabi ba boko ne ke juya akalar Kano – Hadimin Ganduje

Published

on

Hadimin Gwamna Ganduje kuma tsohon Kwamishinan ayyuka na Kano, ya ce, wasu tantirai marasa ilimin addini da boko ne ke juya lamuran gwamnati da siyasar Kano.

Ta cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook Injiniya Mu’az Magaji Ɗan sarauniya ya ce, “Jahilci ba ado ba ne, illa ne ga rayuwa da ci gaban zaman lafiyar al’umma”.

A cewar sa, “Jiha kamar Kano mai PhD Gwamna mai ilimin boko da addini”.

Ya ci gaba da cewa, “Amma a ce wasu tantirai ba arabi ba boko su ne ke juya akalar lamuran mu a siyasa da rayuwa”.

Ƙarin labarai:

Ina fatan mutuwa ta zama silar sulhun Kwankwaso da Ganduje – Ɗan Sarauniya

Abdullahi Abbas bai cancanci shugabancin jam’iyya ba – Ɗan Sarauniya

Wannan magana ta Ɗan Sarauniya ta haifar da kace-nace inda ya fara samun martani daga masu bibiyar shafin nasa.

Wani mai suna Deedat Assumaily ya ce “Mu’azu Magaji don Allah a dinga haƙuri”.

Shi kuma Hassan Cikinza Rano cewa ya yi, “Kuma wallahi yadda suka dama haka zaka sha”.

Sai Abubakar Inuwa Gama, da ya ce, “Win Win faɗa musu gaskiya”.

Ra’ayin Sani Aminu Ladan Ƙoƙi kuma cewa ya yi’ “Ƙwarai kuwa”.

A ranar Litinin ma dai Ɗan Sarauniya ya ƙalubalanci shugaban jam’iyyar APC na Kano Abdullahi Abbas da ya je ayi masa gwajin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

Batun da ya ɗauki hankulan jama’a musamman a kafafen sada zumunta, sai dai har kawo wannan lokaci ba a ji martani daga ɓangaren APC ba game da batutuwan da Ɗan Sarauniyar ke wallafawa.

A shekarar da ta gabata ne Gwamna Ganduje ya sauke shi daga Kwamishina, bayan wasu kalamai da ya yi a Facebook kan mutuwar shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin tarayya Malam Abba Kyari.

Daga baya ne kuma, Ganduje ya sake naɗa shi a matsayin mai sanya ido kan aikin janyo bututun gas zuwa Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!