Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Magu ya shaki iskar ‘yanci

Published

on

Dakataccen shugaban hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati EFCC, Ibrahim Magu ya shaki iskar ‘yanci

Rahotanni sun ce an sako Ibrahim Magu da yammacin ranar Laraba.

A makon jiya ne jami’an tsaron farin kaya suka tsare Ibrahim Magun, bayan da tun farko suka gayyace shi.

Tun daga lokacin ne ya fara bayyana gaban kwamitin fadar shugaban kasa domin kare kansa, game da wasu tuhume-tuhume da ake masa na zargin aikata rashawa.

A cewar rahotanni ofishin ministan shari’a Abubakar Malami na zargin Ibrahim Magu da nuna rashin da’a ga magabatansa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!