Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Kano:APC ta musanta zargin sauya ra’ayin kotun daukaka kara

Published

on

Jamiyyar APC ta musanta zargin da jamiyyar mai hammaya ta PDP ke yi mata na yunkurin amfani alkalan da zasu saurari karar zaben gwamna daza’a gudanar a Kaduna.

Jaridar KanoFocus ta rawaito cewar idan za’a iya tunawa jam’iyyar PDP ta bayyana wannan zargi na ta ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar lahadi din da ta gabata.

Kwamishinan yada labarai Muhammad Garba ne ya bayyana zargin da jamiyyar PDP ke yi a matsayin , cewar ba gaskiya ba ce wani yunkuri ne na shafa jamiyyar APC kashin kaza domin aga baiken ta a idon al’ummar jihar Kano, tare da shafawa kotun daukaka kara laifin .

Mal Muhammad Garba a cikin sanarwa ya bayyana cewa ko a jiya litini da jamiyyar PDP ke yada wannan sanarwa mai ciki da Kazafi, kuma takan yi haka ne da zarar ta fuskanci cewar ba zata yi nasara ba .

Shariar Ganduje da Abba: Jamiyyar PDP na zargin sauya Alkalai

Ya ce APC da dan takarar ta suna da yakinin sakamakon da za’a samu bayan sauraron karar a kotun daukaka kara za’a gudanar da shi cikin adalci ne .

Ya ce gwamnatin jihar Knao ba zata yarda jamiyyar PDP ta haifar da abinda zai kawo rudani da tada zaune tsaye ba kamar yadda sanarwa ta bayyana.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!